Full width home advertisement

Travel the world

Climb the mountains

Post Page Advertisement [Top]

Barcelona zata siyo Ighalo dan ya maye mata gurbin Suarez

Shahararriyar Kungiyar kwallon kafa ta kasar Sifaniya Barcelona ta fara duba yiyuwar sayen dan wasan Najeriya dake bugawa kungiyar Changchun Yatai ta kasar China wasa, Odion Ighalo dan ya zamar mata wanda zata rika canja dan wasanta Suarez dashi.
Barca na neman Ighalone tsohon dan wasan Watford saboda me ci mata kwallo Suarez na daf da daina buga wasa sannan kuma Munir zai bar kungiyar zuwa karshen watannan, hadi da cewa basu so su kashe kudi da yawa wajan sayen sabon dan wasa wanda zasu rika canjashi da Suarez yanda shi Suarez din zai zama sai idan za'a buga babban wasane zasu rika sakashi.
Sport ta ruwaito cewa, Barca ta dade tana bibiyar Ighalo amma bata fito da maitarta fili ba sai yanzu.
Shidai Suarez ya bayyana yanda yake ji da neman madadinshi da Barca take bayan da yaci kwallaye uku a wasan da suka buga da Real Madrid wanda ya kare Barca na cin Madrid 5-1 a watan Octoba na shekarar 2018 da ta gabata inda yace, yana farin ciki da kwallayen da yaci amma fa Barca basu nuna mai cewa yana daya daga cikin fitattun masu cin kwallo na Duniya ba.
Ya kara da cewa ya fahimci neman madadinshi da suke saboda yanzu shekarunshi 31.
Ighalo dai yayi bakin jini ga 'yan Najeriya a wasan da Najeriyar ta buga da kasar Argentina a gasar cin kofin Duniya na shekarar 2018 da aka buga a kasar Rasha saboda damarmakin daya barar.

No comments:

Post a Comment

Bottom Ad [Post Page]

| Designed by Colorlib | Distributed By Best BlogSpot Templates