Travel the world
Climb the mountains
Post Page Advertisement [Top]
Labarai
Hedimasta Ya Yi Wa Daliba 'Yar Shekara Goma Fyade Sauda Dama A Cikin Aji A Garin Danjar Jihar Katsina
Wani hedimasta na makarantar firamare ta Alhazawa dake karamar hukumar Danja a jihar Katsina, mai suna Kabiru Husaini yana ci gaba da zama a gidan kaso biyo bayan zarginsa da yi wa yarinya daliba 'yar shekara goma fyade.
Hedimastan, wanda mazaunin Sabon Gari ne dake garin Zaria, rahotanni sun nuna cewa ya jima yana amfani da yarinyar a cikin ajujuwan makarantar.
Mahaifin yarinyar, shi ya gano hakan a ranar 26 ga watan Janairu, 2020.
Hedimastan dai zai ci gaba da zama a gidan kaso har zuwa ranar 14 ga watan Afrilu, 2020 kafin gurfanar da shi a gaban kotun majestiri karkashin jagorancin Hajiya Fadile Dikko.
Hey there, We are Blossom Themes! We are trying to provide you the new way to look and use the blogger templates. Our designers are working hard and pushing the boundaries of possibilities to widen the horizon of the regular templates and provide high quality blogger templates to all hardworking bloggers!
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
No comments:
Post a Comment